Ayu 7
7
Ayuba Ya Damu da Abin da Allah Ya Yi
1“Kamar kamen soja na tilas,
Haka zaman 'yan adam take,
Kamar zaman mai aikin bauta.
2Kamar bawa ne wanda yake sa zuciya ga inuwa mai sanyi,
Kamar ma'aikaci wanda yake sa zuciya ga lokacin biya.
3Wata da watanni ina ta aikin banza,
Kowane dare ɓacin rai yake kawo mini.
4Sa'ad da na kwanta barci, sai daren ya daɗa tsawo
In yi ta jujjuyawa duk dare, in ƙosa gari ya waye.
5Jikina cike yake da tsutsotsi,
Ƙuraje duka sun rufe shi,
Daga miyakuna mugunya tana ta zuba.
6Kwanakina sun wuce ba sa zuciya,
Sun wuce da sauri kamar ƙoshiyar saƙa.
7“Ka tuna, ya Ubangiji, raina iska ne kawai,
Farin cikina ya riga ya ƙare.
8Kuna ganina yanzu, amma ba za ku sāke ganina ba.
Idan kuka neme ni, za ku tarar ba na nan.
9Kamar girgijen da yake bajewa ya tafi,
Haka nan mutum yake mutuwa.
10Ba kuwa zai ƙara komowa ba,
Mutanen da suka san shi, duka za su manta da shi.
11A'a, ko kaɗan ba zan yi shiru ba!
Haushi nake ji, zuciyata ta ɓaci,
Dole ne in yi magana.
12“Ya Ubangiji, don me ka sa ni a waƙafi?
Kana tsammani ni dodon ruwa ne?
13Na kwanta ina ƙoƙari in huta,
Ina neman taimako don azabar da nake sha.
14Amma kai kana firgita ni da mafarkai,
Kana aiko mini da wahayi da ganegane,
15Har nakan fi so a rataye ni,
Gara in mutu da in rayu a wannan hali.
16Na fid da zuciya. Na gaji da rayuwa.
Ku rabu da ni. Rayuwa ba ta da wata ma'ana.
17 #
Zab 8.4; 144.3 “Ya Ubangiji, me ya sa mutum yake da daraja haka a gare ka?
Me ya sa kake lura da abin da yake yi?
18Kakan dube shi kowace safiya.
Kana jarraba shi a kowane daƙiƙa.
19Ba za ka ko ɗan kawar da kai ba,
Don in samu in haɗiye yau?
20Ko na yi zunubi ina ruwanka,
Kai mai ɗaure mutane?
Me ya sa ka maishe ni abin bārata?
Ni wani babban kaya mai nauyi ne a gare ka?
21Ba za ka iya gafarta mini zunubina ba?
Ba za ka kawar da kai ga muguntar da na aikata ba?
Ba da daɗewa ba zan rasu in koma a ƙura,
Lokacin da ka neme ni ba za ka same ni ba.”
Currently Selected:
Ayu 7: HAU
Highlight
Copy
Compare
Share
Want to have your highlights saved across all your devices? Sign up or sign in
@Bible Society of Nigeria 1979