Ayu 6
6
Ayuba Ya Zargi Abokansa
1Ayuba ya amsa.
2“In da za a auna wahalata da ɓacin raina da ma'auni,
3Da sun fi yashin teku nauyi.
Kada ka yi mamaki da maganganun da nake yi.
4Allah Maɗaukaki ya harbe ni da kibau,
Dafinsu kuwa ya ratsa jikina.
Allah ya jera mini abubuwa masu banrazana.
5“Idan jaki ya sami ciyawar ci, muradinsa ya biya,
In ka ji saniya ta yi shiru, tana cin ingirici ne.
6Amma wane ne zai iya cin abinci ba gishiri?
Akwai daɗin ɗanɗano ga farin ruwan ƙwai?
7Ba na jin marmarin cin abinci irin haka,
Kowane irin abu da na ci yakan sa mini cuta.
8“Me ya sa Allah ya ƙi ba ni abin da nake roƙo?
Me ya sa ya ƙi yin abin da nake so?
9Da ma ya ci gaba kawai ya kashe ni,
Ko ya sake ikonsa ya datse ni!
10Da na san zai yi haka, da sai in yi tsalle don murna,
Da ba zan kula da tsananin azabar da nake ciki ba.
Ban taɓa yin gāba da umarnan Allah ba.
11Wane ƙarfi ne nake da shi na rayuwa?
Wane sa zuciya kuma nake da ita,
tun da na tabbata mutuwa zan yi?
12Da dutse aka yi ni?
Ko da tagulla aka yi jikina?
13Ba ni da sauran ƙarfi da zan ceci kaina,
Ba inda zan juya in nemi taimako.
14“A cikin irin wannan wahala
Ina bukatar amintattun abokai,
Ko da na rabu da Allah, ko ina tare da shi.
15Amma ku abokaina, kun ruɗe ni,
Kamar rafi wanda yakan ƙafe da rani.
16-17Rafin yana cike da iska mai laima da ƙanƙara,
Amma lokacin zafi sai su ɓace,
Kwacciyar rafin, sai ta bushe ba kome.
18Ayari sukan ɓata garin neman ruwa,
Su yi ta gilo, har su marmace a hamada.
19Ayari daga Sheba da Tema suka yi ta nema,
20Amma sa zuciyarsu ta ƙare a gefen busassun rafuffuka,
21Kamar rafuffukan nan kuke a gare ni,
Kun ga abin da ya same ni, kun gigita.
22Na roƙe ku ku ba ni kyauta ne?
Ko kuwa na roƙe ku ku ba wani rashawa domina?
23Ko kuma na roƙe ku ku cece ni daga maƙiyi ko azzalumi ne?
24“To, sai ku koya mini, ku bayyana mini laifofina,
Zan yi shiru in kasa kunne gare ku.
25Kila muhawara mai ma'ana ta rinjaye ni,
Amma yanzu duk maganar shirme kuke yi.
26Kuna so ku amsa maganganuna?
Don me?
Mutumin da yake cikin halin ƙaƙa naka yi,
Ba wata maganar da zai yi in ba shirme ba.
27Kukan jefa wa bayi da marayu kuri'a,
Kukan arzuta kanku daga abokanku na kurkusa.
28Ku dubi fuskata,
Lalle ba zan faɗi ƙarya ba.
29Kai, kun zaƙe, ku daina aikata rashin adalci,
Kada ku sa mini laifi, nake da gaskiya.
30Amma duk da haka kuna tsammani ƙarya nake yi.
Kuna tsammani ba zan iya rarrabe tsakanin gaskiya da ƙarya ba.”
Currently Selected:
Ayu 6: HAU
Highlight
Copy
Compare
Share
Want to have your highlights saved across all your devices? Sign up or sign in
@Bible Society of Nigeria 1979