Ish 62
62
1Zan yi magana domin in ƙarfafa Urushalima,
Ba zan yi shiru ba,
Sai na ga adalcinta ya bayyana kamar haske,
Cetonta kuma ya haskaka kamar fitila da dare.
2Ya Urushalima, al'ummai za su ganki mai gaskiya!
Dukan sarakunansu za su ga darajarki.
Za a kira ki da sabon suna,
Sunan da Ubangiji ya bayar da kansa.
3Za ki zama kamar kyakkyawan rawani ga Ubangiji,
Wato kambin sarauta mai daraja gare shi.
4Ba za a ƙara ce da ke, “Yasasshiya” ba,
Ko a ce da ƙasarki, “Mata wadda Mijinta ya Rabu da Ita.”
Sabon sunanki yanzu shi ne, “Wadda Allah ya Yarda da Ita.”
Ƙasarki kuwa za a ce da ita, “Ta yi Aure da Farin Ciki,”
Domin Ubangiji ya ji daɗinki,
Zai kuwa zama kamar miji ga ƙasarki.
5Ubangiji zai ɗauke ki amaryarsa,
Za ku yi murna tare,
Kamar murnar amarya da ango.
6Ya Urushalima, na sa matsara a garukanki
Ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana.
Za su tuna wa Ubangiji da alkawaransa,
Ba kuwa za su bari ya manta ba!
7Ba za su bari ya huta ba, sai ya ceci Urushalima tukuna,
Ya sa ta zama birnin da dukan duniya za ta yaba wa.
8Ubangiji ya yi alkawari mai ƙarfi,
Ta wurin ikonsa kuwa zai cika shi.
“Hatsinku ba zai ƙara zama abincin abokan gābanku ba,
Baƙi ba za su ƙara shanye ruwan inabinku ba.
9Amma ku da kuka shuka hatsin kuka kuma girbe shi,
Za ku ci abinci, ku yi yabon Ubangiji!
Ku da kuka lura da itatuwan inabi kuka tara su,
Za ku sha ruwan inabi a filayen Haikalina.”
10Ku mutanen Urushalima, ku fita daga cikin birni,
Ku gyara hanyoyi domin jama'arku da suke komowa!
Ku shirya babbar hanya,
Ku kawar da duwatsu daga hanyar!
Ku sa alama domin al'ummai su sani,
11 #
Ish 40.10; W.Yah 22.12 Ubangiji yana sanarwa ga dukan duniya,
Cewa, “Ku ce wa jama'ar Urushalima,
Ubangiji Mai Cetonku yana zuwa,
Yana kawo mutanen da ya cece su.”
12Za a ce da ku, “Tsattsarkar Jama'ar Allah,”
“Jama'ar da Ubangiji ya Fansa!”
Za a kira Urushalima, “Birnin da Allah yake Ƙauna,”
“Birnin da Allah bai Yashe shi Ba.”
Currently Selected:
Ish 62: HAU
Highlight
Share
Copy
Want to have your highlights saved across all your devices? Sign up or sign in
@Bible Society of Nigeria 1979