Zab 70
70
Addu'ar Neman Kuɓuta
1Ka cece ni, ya Allah!
Ya Ubangiji, ka yi hanzari ka taimake ni!
2Ka sa masu so su kashe ni,
A ci nasara a kansu, su ruɗe!
Ka sa waɗanda suke murna saboda wahalaina, su koma baya, su sha kunya!
3Ka sa waɗanda suke mini ba'a
Su razana sabili da fāɗuwarsu!
4Ka sa dukan waɗanda suke zuwa gare ka
Su yi murna, su yi farin ciki!
Ka sa waɗanda suke ƙaunar cetonka
Kullayaumi su ce, “Allah da girma yake!”
5Ba ni da ƙarfi, ba mataimaki,
Ya Allah, ka zo wurina da hanzari.
Kai ne mataimakina da Mai Cetona,
Kada ka yi jinkiri, ya Ubangiji!
Currently Selected:
Zab 70: HAU
Highlight
Copy
Compare
Share
Want to have your highlights saved across all your devices? Sign up or sign in
@Bible Society of Nigeria 1979
Zab 70
70
Addu'ar Neman Kuɓuta
1Ka cece ni, ya Allah!
Ya Ubangiji, ka yi hanzari ka taimake ni!
2Ka sa masu so su kashe ni,
A ci nasara a kansu, su ruɗe!
Ka sa waɗanda suke murna saboda wahalaina, su koma baya, su sha kunya!
3Ka sa waɗanda suke mini ba'a
Su razana sabili da fāɗuwarsu!
4Ka sa dukan waɗanda suke zuwa gare ka
Su yi murna, su yi farin ciki!
Ka sa waɗanda suke ƙaunar cetonka
Kullayaumi su ce, “Allah da girma yake!”
5Ba ni da ƙarfi, ba mataimaki,
Ya Allah, ka zo wurina da hanzari.
Kai ne mataimakina da Mai Cetona,
Kada ka yi jinkiri, ya Ubangiji!
@Bible Society of Nigeria 1979