1
Ish 25:1
Littafi Mai Tsarki
HAU
Ya Ubangiji, kai ne Allahna, Zan ɗaukaka ka, in yabi sunanka. Ka aikata al'amura masu banmamaki, Ka tafiyar da su da aminci, Wato bisa ga shirin da ka yi tuntuni.
Compare
Explore Ish 25:1
2
Ish 25:8
Ubangiji zai hallaka mutuwa har abada! Zai share hawaye daga idanun kowane mutum, ya kawar da kunyar da jama'arsa suke sha a duniya duka. Ubangiji ne da kansa ya faɗa!
Explore Ish 25:8
3
Ish 25:9
Sa'ad da wannan ya faru, kowa zai ce, “Shi Allahnmu ne! Mun dogara gare shi, ya kuwa cece mu. Shi ne Ubangiji. Mun dogara gare shi, yanzu kuwa muna da farin ciki domin ya cece mu!”
Explore Ish 25:9
4
Ish 25:7
A can ne zai kawar da baƙin cikin da ya lulluɓe dukan sauran al'umma.
Explore Ish 25:7
5
Ish 25:6
A kan Dutsen Sihiyona Ubangiji Mai Runduna zai shirya wa dukan sauran al'umman duniya biki da abinci irin na adaras da ruwan inabi mafi kyau.
Explore Ish 25:6
Home
Bible
Plans
Videos