Ish 2
2
Madawwamin Mulkin Salama
(Mika 4.1-3)
1Ga jawabin da Allah ya faɗa wa Ishaya ɗan Amoz a kan Yahuza da Urushalima.
2A kwanaki masu zuwa,
Dutse inda aka gina Haikali zai zama mafi tsayi duka.
Al'ummai da yawa za su zo su yi ta bumbuntowa su zo gare shi.
3Jama'arsu za su ce,
“Bari mu haura zuwa tudun Ubangiji,
Zuwa ga Haikalin Allah na Isra'ila.
Za mu koyi abin da yake so mu yi,
Za mu yi tafiya a hanyar da ya zaɓa.
Koyarwar Ubangiji daga Urushalima take zuwa,
Daga Sihiyona yake magana da jama'arsa.”
4 #
Yow 3.10; Mika 4.3 Zai sulhunta jayayyar da yake tsakanin manyan al'ummai,
Za su mai da takubansu garemani,
Masunsu kuma su maishe su wuƙaƙen aske itace,
Al'ummai ba za su ƙara fita zuwa yaƙi ba,
Ba za su ƙara koyon yaƙi ba.
Hukuncin Allah a kan Masu Girmankai
5Yanzu fa, zuriyar Yakubu, bari mu yi tafiya a cikin hasken da Ubangiji ya ba mu!
6Ya Allah, ka rabu da jama'arka, zuriyar Yakubu. Ƙasa ta cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas, daga kuma ƙasar Filistiya. Jama'a suna bin baƙin al'adu. 7Ƙasarsu tana cike da azurfa da zinariya, dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu tana cike da dawakai, karusansu kuma ba iyaka. 8Ƙasarsu tana cike da gumaka, suna sujada ga abubuwan da suka yi da hannuwansu.
9Za a ƙasƙantar da kowane mutum, a kunyata shi. Kada ka gafarta musu, ya Ubangiji!
10 #
W.Yah 6.15; 2Tas 1.9 Za su ɓuya a cikin kogwannin duwatsu, ko su haƙa ramummuka a ƙasa, suna ƙoƙarin tserewa daga fushin Ubangiji, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa! 11Rana tana zuwa sa'ad da girmankan 'yan adam zai ƙare, zai kuma lalatar da fāriyar 'yan adam. Sa'an nan Ubangiji ne kaɗai za a ɗaukaka. 12A wannan rana, Ubangiji Mai Runduna zai ƙasƙantar da kowane mai iko, da kowane mai girmankai, da kowane mai fāriya. 13Zai hallaka dogayen itatuwan al'ul na Lebanon, da dukan itatuwan oak na ƙasar Bashan. 14Zai baje duwatsu da tuddai masu tsayi, 15da kowace doguwar hasumiya, da ganuwar kowace kagara. 16Zai nutsar da jiragen ruwa mafi girma mafi kyau. 17Girmankan ɗan adam zai ƙare, za a hallakar da fāriyar ɗan adam, Ubangiji ne kaɗai za a ɗaukaka sa'ad da wannan rana ta yi, 18za a shafe gumaka ƙaƙaf.
19Mutane za su ɓuya a kogwannin duwatsu, ko su haƙa ramummuka a ƙasa, suna ƙoƙarin tserewa daga fushin Ubangiji, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa, sa'ad da ya zo domin ya girgiza duniya. 20Sa'ad da wannan rana ta yi za su zubar da gumakan da suka yi na zinariya da azurfa, za su bar wa ɓeraye da jemagu. 21Sa'ad da Ubangiji ya zo domin ya girgiza duniya, jama'a za su ɓuya a cikin kogwannin tuddai da ramummukan duwatsu, suna ƙoƙari su ɓuya daga fushinsa, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa.
22Kada ku dogara ga 'yan adam. Wace daraja take gare su?
Currently Selected:
Ish 2: HAU
Highlight
Share
Copy
Want to have your highlights saved across all your devices? Sign up or sign in
@Bible Society of Nigeria 1979
Ish 2
2
Madawwamin Mulkin Salama
(Mika 4.1-3)
1Ga jawabin da Allah ya faɗa wa Ishaya ɗan Amoz a kan Yahuza da Urushalima.
2A kwanaki masu zuwa,
Dutse inda aka gina Haikali zai zama mafi tsayi duka.
Al'ummai da yawa za su zo su yi ta bumbuntowa su zo gare shi.
3Jama'arsu za su ce,
“Bari mu haura zuwa tudun Ubangiji,
Zuwa ga Haikalin Allah na Isra'ila.
Za mu koyi abin da yake so mu yi,
Za mu yi tafiya a hanyar da ya zaɓa.
Koyarwar Ubangiji daga Urushalima take zuwa,
Daga Sihiyona yake magana da jama'arsa.”
4 #
Yow 3.10; Mika 4.3 Zai sulhunta jayayyar da yake tsakanin manyan al'ummai,
Za su mai da takubansu garemani,
Masunsu kuma su maishe su wuƙaƙen aske itace,
Al'ummai ba za su ƙara fita zuwa yaƙi ba,
Ba za su ƙara koyon yaƙi ba.
Hukuncin Allah a kan Masu Girmankai
5Yanzu fa, zuriyar Yakubu, bari mu yi tafiya a cikin hasken da Ubangiji ya ba mu!
6Ya Allah, ka rabu da jama'arka, zuriyar Yakubu. Ƙasa ta cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas, daga kuma ƙasar Filistiya. Jama'a suna bin baƙin al'adu. 7Ƙasarsu tana cike da azurfa da zinariya, dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu tana cike da dawakai, karusansu kuma ba iyaka. 8Ƙasarsu tana cike da gumaka, suna sujada ga abubuwan da suka yi da hannuwansu.
9Za a ƙasƙantar da kowane mutum, a kunyata shi. Kada ka gafarta musu, ya Ubangiji!
10 #
W.Yah 6.15; 2Tas 1.9 Za su ɓuya a cikin kogwannin duwatsu, ko su haƙa ramummuka a ƙasa, suna ƙoƙarin tserewa daga fushin Ubangiji, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa! 11Rana tana zuwa sa'ad da girmankan 'yan adam zai ƙare, zai kuma lalatar da fāriyar 'yan adam. Sa'an nan Ubangiji ne kaɗai za a ɗaukaka. 12A wannan rana, Ubangiji Mai Runduna zai ƙasƙantar da kowane mai iko, da kowane mai girmankai, da kowane mai fāriya. 13Zai hallaka dogayen itatuwan al'ul na Lebanon, da dukan itatuwan oak na ƙasar Bashan. 14Zai baje duwatsu da tuddai masu tsayi, 15da kowace doguwar hasumiya, da ganuwar kowace kagara. 16Zai nutsar da jiragen ruwa mafi girma mafi kyau. 17Girmankan ɗan adam zai ƙare, za a hallakar da fāriyar ɗan adam, Ubangiji ne kaɗai za a ɗaukaka sa'ad da wannan rana ta yi, 18za a shafe gumaka ƙaƙaf.
19Mutane za su ɓuya a kogwannin duwatsu, ko su haƙa ramummuka a ƙasa, suna ƙoƙarin tserewa daga fushin Ubangiji, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa, sa'ad da ya zo domin ya girgiza duniya. 20Sa'ad da wannan rana ta yi za su zubar da gumakan da suka yi na zinariya da azurfa, za su bar wa ɓeraye da jemagu. 21Sa'ad da Ubangiji ya zo domin ya girgiza duniya, jama'a za su ɓuya a cikin kogwannin tuddai da ramummukan duwatsu, suna ƙoƙari su ɓuya daga fushinsa, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa.
22Kada ku dogara ga 'yan adam. Wace daraja take gare su?
Currently Selected:
:
Highlight
Share
Copy
Want to have your highlights saved across all your devices? Sign up or sign in
@Bible Society of Nigeria 1979