Amma da alheri da kuma ƙaunar Allah Mai Cetonmu suka bayyana, sai ya cece mu, ba saboda abubuwan adalcin da muka aikata ba, sai dai saboda jinƙansa. Ya cece mu ta wurin wankan nan na sāke haihuwa da kuma sabuntawan nan ta Ruhu Mai Tsarki, wanda ya zubo mana a yalwace ta wurin Yesu Kiristi Mai Cetonmu, wannan fa domin an kuɓutar da mu ne ta wurin alherinsa, don mu zama magāda masu begen ga rai madawwami.