1
Fit 20:2-3
Littafi Mai Tsarki
HAU
“Ni ne Ubangiji Allahnka wanda ya fisshe ka daga ƙasar Masar, daga gidan bauta. “Kada ka kasance da waɗansu alloli sai ni.
Sammenlign
Utforsk Fit 20:2-3
2
Fit 20:4-5
“Kada ka yi wa kanka wani gunki ko kuwa wata siffa ta wani abu a sama a bisa, ko a duniya a ƙasa, ko kuma a ruwa a ƙarƙarshin ƙasa. Kada ka rusuna musu, kada kuwa ka bauta musu, gama ni Ubangiji Allahnka, mai kishi ne. Nakan hukunta 'ya'ya har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suke ƙina.
Utforsk Fit 20:4-5
3
Fit 20:12
“Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, domin ka yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
Utforsk Fit 20:12
4
Fit 20:8
“Tuna da rana Asabar, ka kiyaye ta da tsarki.
Utforsk Fit 20:8
5
Fit 20:7
“Kada ka kama sunan Ubangiji Allahnka a banza, gama zan hukunta duk wanda ya kama sunana a banza.
Utforsk Fit 20:7
6
Fit 20:9-10
Za ku yi dukan ayyukanku cikin kwana shida, amma rana ta bakwai keɓaɓɓiya ce ga Ubangiji Allahnka. A ranar ba za ka yi kowane irin aiki ba, ko kai, ko 'ya'yanka, ko barorinka, ko dabbobinka, ko kuwa baƙon da yake zaune tare da ku.
Utforsk Fit 20:9-10
7
Fit 20:17
“Kada ka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka. Kada kuma ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka, ko barorinsa mata da maza, ko sansa, ko jakinsa, ko kowane abin da yake nasa.”
Utforsk Fit 20:17
8
Fit 20:16
“Kada ka ɓāta sunan maƙwabcinka.
Utforsk Fit 20:16
9
Fit 20:14
“Kada ka yi zina.
Utforsk Fit 20:14
10
Fit 20:13
“Kada ka yi kisankai.
Utforsk Fit 20:13
11
Fit 20:15
“Kada ka yi sata.
Utforsk Fit 20:15