L.Ƙid 10
10
Kakaki na Azurfa
1Ubangiji kuma ya ce wa Musa, 2“Ka ƙera kakaki biyu na azurfa don ka riƙa kirawo taron jama'a, don kuma ka riƙa sanashe su lokacin tashi daga zangon. 3Lokacin da aka busa kakaki biyu ɗin gaba ɗaya, sai taron jama'a duka su tattaru a wurinka a ƙofar alfarwa ta sujada. 4Amma idan ɗaya kaɗai aka busa, sai shugabannin Isra'ila su tattaru a wurinka. 5Sa'ad da kuka yi busar faɗakarwa, waɗanda suke zaune a gabashin zangon za su tashi. 6Sa'ad da kuma kuka yi busar faɗakarwa ta biyu, waɗanda suke a kudancin zangon za su tashi. Sai a yi busar faɗakarwa a kowane lokaci da za su tashi. 7Amma idan za a kira jama'a ne sai a yi busa da ƙarfi amma banda faɗakarwa. 8'Ya'yan Haruna, maza, firistoci, su ne za su busa kakakin.
“Kakakin za su zama muku ka'ida ta din din din cikin dukan zamananku. 9Sa'ad da kuka tafi yaƙi a ƙasarku gāba da maƙiyanku da suke matsa muku lamba, sai ku yi busar faɗakarwan nan da kakakin, Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, ya cece ku daga maƙiyanku. 10A ranar murnarku, da lokacin ƙayyadaddun idodinku, da tsayawar watanninku, za ku busa kakakin a lokacin yin hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama. Za su zama sanadin tunawa da ku a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Tashin Isra'ilawa daga Sinai
11A rana ta ashirin ga watan biyu a shekara ta biyu, sai aka gusar da girgijen daga kan alfarwa ta sujada. 12Isra'ilawa kuwa suka tashi daki-daki daga jejin Sinai. Girgijen kuma ya tsaya a jejin Faran. 13Suka fara tafiyarsu bisa ga umarnin da Ubangiji ya yi wa Musa. 14Tutar zangon kabilar mutanen Yahuza ta fara tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Nashon, ɗan Amminadab, shi ne shugaban rundunarsu. 15Shugaban rundunar kabilar mutanen Issaka Netanel ne, ɗan Zuwar. 16Shugaban rundunar kabilar mutanen Zabaluna Eliyab ne, ɗan Helon.
17Sa'an nan aka kwankwance alfarwar, sai 'ya'yan Gershon, da 'ya'yan Merari masu ɗaukar alfarwar suka kama hanya.
18Tutar zangon kabilar mutanen Ra'ubainu ta tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Shugaban rundunarsu Elizur ne, ɗan Shedeyur. 19Shugaban rundunar kabilar mutanen Saminu kuwa Shelumiyel ne, ɗan Zurishaddai. 20Shugaban rundunar kabilar mutanen Gad Eliyasaf ne, ɗan Deyuwel.
21Daga nan sai Kohatawa masu ɗauke da kayayyaki masu tsarki suka tashi. Kafin su isa masaukin, an riga an kafa alfarwar.
22Tutar zangon mutanen Ifraimu ta tashi, ƙungiyoyinsu na biye. Shugaban rundunarsu Elishama ne, ɗan Ammihud. 23Shugaban rundunar kabilar mutanen Manassa Gamaliyel ne, ɗan Fedazur. 24Shugaban rundunar kabilar mutanen Biliyaminu Abidan ne, ɗan Gideyoni.
25A ƙarshe sai ƙungiyar mutanen Dan da take bayan dukan zangon, ta tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Shugaban rundunarsu Ahiyezer ne, ɗan Ammishaddai. 26Shugaban rundunar kabilar mutanen Ashiru Fagiyel ne, ɗan Okran. 27Shugaban rundunar kabilar mutanen Naftali Ahira ne, ɗan Enan. 28Wannan shi ne tsarin tafiyar Isra'ilawa bisa ga rundunansu sa'ad da sukan tashi.
29Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamadayane, surukinsa, “Muna kan hanya zuwa wurin da Ubangiji ya ce zai ba mu, ka zo tare da mu, za mu yi maka alheri, gama Ubangiji ya alkawarta zai yi wa Isra'ila alheri.”
30Amma ya ce masa, “Ba zan tafi ba, zan koma ƙasata da wurin dangina.”
31Musa kuwa ya ce masa, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu, gama ka san jejin da muke zango, kai za ka zama idonmu. 32Idan ka tafi tare da mu, kowane irin alheri da Ubangiji zai yi mana, mu kuma haka za mu yi maka.”
Mutanen suka Kama Hanya
33Sai suka tashi daga dutsen Ubangiji, wato Sinai, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji kuwa ya wuce gabansu don ya nemar musu masauki.
34A duk lokacin da suka tashi daga zango, sai girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
35 #
Zab 68.1
Duk kuma lokacin da akwatin zai tashi, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji, ka sa maƙiyanka su warwatse, ka sa waɗanda suke ƙinka su gudu gabanka.” 36Sa'ad da akwatin ya sauka kuma, Musa yakan ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubun dubbai na iyalan Isra'ila.”
Currently Selected:
L.Ƙid 10: HAU
Highlight
Copy
Compare
Share
Want to have your highlights saved across all your devices? Sign up or sign in
@Bible Society of Nigeria 1979
L.Ƙid 10
10
Kakaki na Azurfa
1Ubangiji kuma ya ce wa Musa, 2“Ka ƙera kakaki biyu na azurfa don ka riƙa kirawo taron jama'a, don kuma ka riƙa sanashe su lokacin tashi daga zangon. 3Lokacin da aka busa kakaki biyu ɗin gaba ɗaya, sai taron jama'a duka su tattaru a wurinka a ƙofar alfarwa ta sujada. 4Amma idan ɗaya kaɗai aka busa, sai shugabannin Isra'ila su tattaru a wurinka. 5Sa'ad da kuka yi busar faɗakarwa, waɗanda suke zaune a gabashin zangon za su tashi. 6Sa'ad da kuma kuka yi busar faɗakarwa ta biyu, waɗanda suke a kudancin zangon za su tashi. Sai a yi busar faɗakarwa a kowane lokaci da za su tashi. 7Amma idan za a kira jama'a ne sai a yi busa da ƙarfi amma banda faɗakarwa. 8'Ya'yan Haruna, maza, firistoci, su ne za su busa kakakin.
“Kakakin za su zama muku ka'ida ta din din din cikin dukan zamananku. 9Sa'ad da kuka tafi yaƙi a ƙasarku gāba da maƙiyanku da suke matsa muku lamba, sai ku yi busar faɗakarwan nan da kakakin, Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, ya cece ku daga maƙiyanku. 10A ranar murnarku, da lokacin ƙayyadaddun idodinku, da tsayawar watanninku, za ku busa kakakin a lokacin yin hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama. Za su zama sanadin tunawa da ku a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Tashin Isra'ilawa daga Sinai
11A rana ta ashirin ga watan biyu a shekara ta biyu, sai aka gusar da girgijen daga kan alfarwa ta sujada. 12Isra'ilawa kuwa suka tashi daki-daki daga jejin Sinai. Girgijen kuma ya tsaya a jejin Faran. 13Suka fara tafiyarsu bisa ga umarnin da Ubangiji ya yi wa Musa. 14Tutar zangon kabilar mutanen Yahuza ta fara tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Nashon, ɗan Amminadab, shi ne shugaban rundunarsu. 15Shugaban rundunar kabilar mutanen Issaka Netanel ne, ɗan Zuwar. 16Shugaban rundunar kabilar mutanen Zabaluna Eliyab ne, ɗan Helon.
17Sa'an nan aka kwankwance alfarwar, sai 'ya'yan Gershon, da 'ya'yan Merari masu ɗaukar alfarwar suka kama hanya.
18Tutar zangon kabilar mutanen Ra'ubainu ta tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Shugaban rundunarsu Elizur ne, ɗan Shedeyur. 19Shugaban rundunar kabilar mutanen Saminu kuwa Shelumiyel ne, ɗan Zurishaddai. 20Shugaban rundunar kabilar mutanen Gad Eliyasaf ne, ɗan Deyuwel.
21Daga nan sai Kohatawa masu ɗauke da kayayyaki masu tsarki suka tashi. Kafin su isa masaukin, an riga an kafa alfarwar.
22Tutar zangon mutanen Ifraimu ta tashi, ƙungiyoyinsu na biye. Shugaban rundunarsu Elishama ne, ɗan Ammihud. 23Shugaban rundunar kabilar mutanen Manassa Gamaliyel ne, ɗan Fedazur. 24Shugaban rundunar kabilar mutanen Biliyaminu Abidan ne, ɗan Gideyoni.
25A ƙarshe sai ƙungiyar mutanen Dan da take bayan dukan zangon, ta tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Shugaban rundunarsu Ahiyezer ne, ɗan Ammishaddai. 26Shugaban rundunar kabilar mutanen Ashiru Fagiyel ne, ɗan Okran. 27Shugaban rundunar kabilar mutanen Naftali Ahira ne, ɗan Enan. 28Wannan shi ne tsarin tafiyar Isra'ilawa bisa ga rundunansu sa'ad da sukan tashi.
29Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamadayane, surukinsa, “Muna kan hanya zuwa wurin da Ubangiji ya ce zai ba mu, ka zo tare da mu, za mu yi maka alheri, gama Ubangiji ya alkawarta zai yi wa Isra'ila alheri.”
30Amma ya ce masa, “Ba zan tafi ba, zan koma ƙasata da wurin dangina.”
31Musa kuwa ya ce masa, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu, gama ka san jejin da muke zango, kai za ka zama idonmu. 32Idan ka tafi tare da mu, kowane irin alheri da Ubangiji zai yi mana, mu kuma haka za mu yi maka.”
Mutanen suka Kama Hanya
33Sai suka tashi daga dutsen Ubangiji, wato Sinai, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji kuwa ya wuce gabansu don ya nemar musu masauki.
34A duk lokacin da suka tashi daga zango, sai girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
35 #
Zab 68.1
Duk kuma lokacin da akwatin zai tashi, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji, ka sa maƙiyanka su warwatse, ka sa waɗanda suke ƙinka su gudu gabanka.” 36Sa'ad da akwatin ya sauka kuma, Musa yakan ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubun dubbai na iyalan Isra'ila.”
Currently Selected:
:
Highlight
Copy
Compare
Share
Want to have your highlights saved across all your devices? Sign up or sign in
@Bible Society of Nigeria 1979